8.4.10

Ina mamakin yadda al'ummar hausawa zata kasance nan da wasu shekaru masu zuwa, kasancewar yadda na ga illimin addini yawaita a tsakanin al'ummar hausawa, ko'ina ka duba sai kaga sabuwar makarantar islamiyya, a zauren gida ne, a cikin gidan matan aure ne har da kofar gidaje a yau zaka ga ana karatun addini. Sannan babu unguwar da zaka shiga a cikin birnin Kano da kewayenta baka ga duk kwararon da ka shiga ko lungu baka ga masallaci akalla guda biyu ba ko da kuwa irin mazaunar nan ce ta hirar samari ko ta 'yan boko da suke haduwa suyi salla. Massalatan Jumma'a kuwa abin kamar bizines nan kaji ana salla karfe daya can kaji daya da rabi suke salla, can kuma karfe biyu ake salla.

Duk da irin wancan cigaban addinin da aka samu a kasar Hausa wanda ba zan ce uffan akai ba, sai gashi mun fi kowa tozarta al'amarin aure da sakaci da tarbiyar 'ya'yanmu wadanda sune jarinmu mafi tsada kuma sune abin alfaharinmu, muna raye ne ko kuwa muna a mace ne. Sannan yana yin neman aurenmu da zamantakewar aurenmu mu da yadda muke tarbiyar 'ya'yanmu mu hausawa a yau tayi nesa da yadda addininmu ya tsara mana mu bi, amma idan an zo maganar addini mun fi kowa daukar zafi a halin gashi mun yiwa addininmu tsira a kasuwa.

A yau duk kasar Najeriya babu wata kabila da take kaunar ta baiwa Malam bahaushe aure saboda yadda ya zama lamba daya wajen tozarta aure. A jaridar Aminiya an taba bada labarin wani mutum mai suna Ali dan kabilar babur daya kashe 'yar sa a dalilin zata auri bahaushe. Yanzu wannan kadai bai isa ya nunawa duniya yadda muka yi watsi da kyawawar al'adar nan ta mu ta rikon aure da tarbiyar 'ya'yanmu ba. A yau a jihata ta Kano sakin aure da zinace-zainace da suke aukuwa tsakanin ofisoshin gwamnati da ma'aikatu da dakunan otal-otal da kuma gidaje a kullum yafi yawan haihuwa da ake yi a kullum! Da wannan irin muguwar dabi'a ce muke tunanin samun zuriya ta gari?

6.12.07

Hana rawar batsa da wakar fajirci da hukumomi a jihata ta Kano suka yi a cikin fina-finan hausa wannan wani yunkuri ne wanda ya zama dole na mikewa tsaye kuma na cirewa hula, sannan na hade hannayena na yiwa tafi, raf! raf! raf!

Babu wani bahaushe musulmi mai salla, mai cikakken hankali da zai amince da irin abin da aka aikata a cikin wakar 'BABBAR RIGA' wadda akayi a fim din Babbar Riga kuma ya amince da cewa wannan waka tayi daidai da addinin mutanen Kano, ko da al'adarsu, wanda wannan waka ita kadai ta isa ta bude kofofin masifu ga al'ummar mutanen Kano domin babu abin da aka nuna a cikin wannan waka face tsantsar fajirci da wulakanta bahaushe da mai dashi wawa mara tunani mara kishin al'ummarsa. Idan ba haka ba ta yaya zai zuba ido wasu banza bakwai su zo har garinsa, su shiga rigarsa, su dauki yaransa su wulakanta shi a idon duniya da sunan nishadantarwa. Dubi yadda aka yi amfani da al'adun bahaushe a wannan wakar, ka ga dai sarautarsa, rawaninsa, fadarsa, rigar mutuncinsa kuma aka zo aka hada da al'adar da bata da tushe hatta a wajen wadanda aka kwaikwaya domin shigar da matan da aka yi wannan waka dasu ko a turawan ma sai tatacciyar 'yar...................... ce zata yi wannan shiga, amma sai gashi a na bayyana wadannan 'yan mata a matsayin hausawa. Shin wannan fim mai dauke da wannan muguwar waka dama ya bi ta hukumar AA Kurawa kuma malaman hukumar sun ga wannan waka kuma suka barta ta shiga kasuwa tun a lokacin?

Bani da wani gilli akan wanda ya shirya wancan fim face dai na san ya wukalanta mini al'adata a matsayinsa na wanda ban taba damuwa da al'adarsa ba ko kabilarsa ba duk dana san suna da miyagun dabi'un da zan iya shirya fim akansu domin daukarwa al'ummata fansa akai amma ni bana jin zan aikata haka

12.11.07

BOBO-HIYANA

salam.
Yan uwana musulmi ina muku barka da warhaka. Naga labarin abin daya faru na hoton bidiyon tsiraici na 'Yar wasan Hausa Maryama Hiyana wanda jaridar almizan ta buga. Lalle almizan nayi mamakin yadda kika bayyana Ibrahim Mandawari a matsayin wani mutumin kirki a halin shine wanda yayi sanadin fadawar wannan yarinya cikin wannan harka ta fitsara wadda ake koyawa yara mata da sunan sana'ar Fina-finan hausa. Abin daya sa na fadi haka kuwa shine, shi dai wancan mutumi, Ibrahim Mandawari shine wanda ya fari waka a cikin Fim din hausa, a wani wasa mai suna Jamila da jamilu wanda daga nan ya bude kofofin wakokin fina-finai wanda a sakamakon haka ya yaudadrar da tunanin matasa masoya Manzon Allah SAWA wadanda suke nishadantar da kuma illimantar da al'umma cikin yabon da suke yi wa shugaban halitta Manzo Muhammad SAWA, wanda saboda akasarin matasan basu samu tarbiyyar ruhi ta gaskiya ba sai suka fada cikin wakokin hausa na soyayya saboda kudaden da suka hangen samu a wannan sabuwar hanya wadda tayi hannun riga da tarbiyyar musulunci, kuma tayi daidai da tarbiyya da al'ada ta masu bautar gumakan Kirishna da Budha dake kasar Indiya, kuma suka dauki salon raye-rayensu da suke yi tsakanin mata da maza wanda ko mahaukaci ya san ya sabawa hanyar tarbiyyar musulunci, amma malamanmu na fada dana zaure dana talabijin da rediyo da shehunanmu duk suka zuba ido suna gani saboda domin su kullum suna hangen abin da ya faru a baya ne ko kuma ake ciki basa hangen gobe kiyama da abin da zai kassance a gobe a gidan duniyar da muke ciki ba.
A shekearun da suka gabata idan ka ji muryar budurwa tana rera wake ka tabbata yabon Manzon Allah SAWA ne da Iyalansa ko sahabbansa, kuma duk wadda ta kware wajen rera yabon Manzon Allah SAWA zaka gani duk muninta rububin aurenta jama'a suke yi domin tayi riko da igiyar da bata rubewa bare ta tsinke, kuma duk zinar mazinaci ba zai yi sha'awar yin lalata da ita ba, domin duk abin da mutum yake so yana tare da shi, masu yabon Manzon Allah SAWA suna tare da Manzon Allah SAWA kuma suna cikin kariyarsa a duniya da lahira. Jama'a ku dubi Shareef Rabiu Usman Baba, ku dubi Mustapha Gadon Kaya, ku dubi Malam Hussain na Shehu Aliyu Harazimi Kano, Ku dubi Hassan Alaye da Bashir Dandago wanda wata yarinya tayi mafarki da Nana Fatima As inda ta fada mata tayiwa Malam Bashir Dandago albishir da gidan aljanna.
Kishiyar wancan zancen nawa sune masu wakokin Fina-finan batsa na Hausa inda zaka ga ana kalaman da ko mahaukaci ya san batsane a cikinsu wanda zaka ji wasu wakokin fitsarane kai tsaye misalinsu sun hada irinsu, "ZUBAR GADO ! wadda Yakubu Mohammed yayi da wakar Shaba, "YI MATA RAWA" da wakar , JAMILA TA IYA DAURA ZANI da wakar BABBAR RIGA wanda Sani Danja yayi su. Zaku amince dani idan kuka ji furucin da wannan mawaka suke yi a cikin wakokinsu wanda kuma ake musu shiga wadda tayi daidai da sakon da suke isarwa zuwa ga al'umma, kuma a cikin irin wannan wakokin ne matan 'yan Fim din batsa na Hausa suke tallan kansu ga masu bukata ta hanyar yin duk wani abun da zai isar da sakon zuciya ga dangin jama'ar Annabi Lud As da muke zaune dasu a wannan kasa. Kuma akasarin masu neman matan nan suna amfani da wayoyin masu sanya su aikata wannan aikin masha'a ne da ake kiransu Darektos wanda suke sanya lambobin wayoyinsu a jikin bangon kwalin kaset din da suka yi, wanda tana nan ne mai bukata zai kulla ciniki da su.
Babu wani mai laifin daya wuce Malam Ibrahim Shekarau a cikin abin da masu Fina-finan hausa suke aikatawa a jihar Kano, domin shine jagoran jihar kuma duk abin daya ke faruwa a jiharsa yana sane da shi, wanda har kyaututtuka yake rabawa 'yan wasan hausa a halin yana sane da irin abin da suke gudanarwa a ciki da wajen jiharsa, kuma hukumar daya kafa ta tace fina-finai wadda take dauke da wasu mutane da ake kira Malamai magada arnan baya wanda sune suke baiwa kowane fim damar fitowa kasuwa idan sun duba shi kuma wai suka tabbatar ya dace da tsarin koyarwar addinin musulunci, ko wadannan magada arnan baya suna ina ne a lokacin da Fim din GUDA ya fito? Kuma suna ina ne Sani Danja ya fitar da Fim dinsa na MAI BABBAR RIGA ? Tabbas lokaci yayi da al'umma zata zabawa kanta mafita ko dai ta bi hanyar Allah SWT wadda yake fawwalawa wasu daga bayinsa wadanda ya zaba su bayyanawa mutane mafita ko kuma su hadu da mutanen Fir'auna da Abu jahil a matattara guda.
Naji ance gwamnatin Kano wai ta dakatar yin Fina-finan batsa na hausa har tsawon watanni uku kuma ta hana rawa da waka a fina-finan hausa, amma gidajen rediyo mallakarta suna nan suna dada tallan wadannan fina-finan batsa na hausa ta hanyar sanya wakokin batsar da suka yi a baya. Shin jagoran Gwamnatin jihar Kano bai san da yunkurin da almajiran Malamin nan na Zariya suka yi ba na yin Fim din Shehu Usman Dan Fodio ba ne ba? Idan ya sani wace irin gudumowa ya bada a matsayinsa na wanda ya amfani jihadin Shehu? Mu ma 'Yan Tijjaniyya muna binsa bashi domin muna da hakkin ya sa ayi mana Fim din Shehu Tijjani domin Malamanmu sun tare a gidansa suna kwadayin abin duniya, har suna zuga shi wai 'Yan Kadiriyya sun zama Shi'a.
Shawarata ga Malam Ibrahim Shekarau itace ya ruguza harkar Fina-finan batsa na hausa har abada, kuma ya hana wakokin soyayya irin nasu har abada, sannan ya nemi mutane masana addini su kirkiri wani abu wanda zai maye waccan muguwar sana'a irinta mutanen Annabi Ludu, kuma ya hana shirin da Ibrahim Mandawari yake gabatarwa a gidan rediyon Freedom dake Kano na Fina-Finan hausa.

RABIU HAMDALA
08065273401

BOBO-HIYANA

salam.

Yan uwana musulmi ina muku barka da warhaka. Naga labarin abin daya faru na hoton bidiyon tsiraici na 'Yar wasan Hausa Maryama Hiyana wanda jaridar almizan ta buga. Lalle almizan nayi mamakin yadda kika bayyana Ibrahim Mandawari a matsayin wani mutumin kirki a halin shine wanda yayi sanadin fadawar wannan yarinya cikin wannan harka ta fitsara wadda ake koyawa yara mata da sunan sana'ar Fina-finan hausa. Abin daya sa na fadi haka kuwa shine, shi dai wancan mutumi, Ibrahim Mandawari shine wanda ya fari waka a cikin Fim din hausa, a wani wasa mai suna Jamila da jamilu wanda daga nan ya bude kofofin wakokin fina-finai wanda a sakamakon haka ya yaudadrar da tunanin matasa masoya Manzon Allah SAWA wadanda suke nishadantar da kuma illimantar da al'umma cikin yabon da suke yi wa shugaban halitta Manzo Muhammad SAWA, wanda saboda akasarin matasan basu samu tarbiyyar ruhi ta gaskiya ba sai suka fada cikin wakokin hausa na soyayya saboda kudaden da suka hangen samu a wannan sabuwar hanya wadda tayi hannun riga da tarbiyyar musulunci, kuma tayi daidai da tarbiyya da al'ada ta masu bautar gumakan Kirishna da Budha dake kasar Indiya, kuma suka dauki salon raye-rayensu da suke yi tsakanin mata da maza wanda ko mahaukaci ya san ya sabawa hanyar tarbiyyar musulunci, amma malamanmu na fada dana zaure dana talabijin da rediyo da shehunanmu duk suka zuba ido suna gani saboda domin su kullum suna hangen abin da ya faru a baya ne ko kuma ake ciki basa hangen gobe kiyama da abin da zai kassance a gobe a gidan duniyar da muke ciki ba.
A shekearun da suka gabata idan ka ji muryar budurwa tana rera wake ka tabbata yabon Manzon Allah SAWA ne da Iyalansa ko sahabbansa, kuma duk wadda ta kware wajen rera yabon Manzon Allah SAWA zaka gani duk muninta rububin aurenta jama'a suke yi domin tayi riko da igiyar da bata rubewa bare ta tsinke, kuma duk zinar mazinaci ba zai yi sha'awar yin lalata da ita ba, domin duk abin da mutum yake so yana tare da shi, masu yabon Manzon Allah SAWA suna tare da Manzon Allah SAWA kuma suna cikin kariyarsa a duniya da lahira. Jama'a ku dubi Shareef Rabiu Usman Baba, ku dubi Mustapha Gadon Kaya, ku dubi Malam Hussain na Shehu Aliyu Harazimi Kano, Ku dubi Hassan Alaye da Bashir Dandago wanda wata yarinya tayi mafarki da Nana Fatima As inda ta fada mata tayiwa Malam Bashir Dandago albishir da gidan aljanna.
Kishiyar wancan zancen nawa sune masu wakokin Fina-finan batsa na Hausa inda zaka ga ana kalaman da ko mahaukaci ya san batsane a cikinsu wanda zaka ji wasu wakokin fitsarane kai tsaye misalinsu sun hada irinsu, "ZUBAR GADO ! wadda Yakubu Mohammed yayi da wakar Shaba, "YI MATA RAWA" da wakar , JAMILA TA IYA DAURA ZANI da wakar BABBAR RIGA wanda Sani Danja yayi su. Zaku amince dani idan kuka ji furucin da wannan mawaka suke yi a cikin wakokinsu wanda kuma ake musu shiga wadda tayi daidai da sakon da suke isarwa zuwa ga al'umma, kuma a cikin irin wannan wakokin ne matan 'yan Fim din batsa na Hausa suke tallan kansu ga masu bukata ta hanyar yin duk wani abun da zai isar da sakon zuciya ga dangin jama'ar Annabi Lud As da muke zaune dasu a wannan kasa. Kuma akasarin masu neman matan nan suna amfani da wayoyin masu sanya su aikata wannan aikin masha'a ne da ake kiransu Darektos wanda suke sanya lambobin wayoyinsu a jikin bangon kwalin kaset din suka yi, wanda tana nan ne mai bukata zai kulla ciniki da su.
Babu wani mai laifin daya wuce Malam Ibrahim Shekarau a cikin abin da masu Fina-finan hausa suke aikatawa a jihar Kano, domin shine jagoran jihar kuma duk abin daya ke faruwa a jiharsa yana sane da shi, wanda har kyaututtuka yake rabawa 'yan wasan hausa a halin yana sane da irin abin da suke gudanarwa a ciki da wajen jiharsa, kuma hukumar daya kafa ta tace fina-finai wadda take dauke da wasu mutane da ake kira Malamai magada arnan baya wanda sune suke baiwa kowane fim damar fitowa kasuwa idan sun duba shi kuma wai suka tabbatar ya dace da tsarin koyarwar addinin musulunci, ko wadannan magada arnan baya suna ina ne a lokacin da Fim din GUDA ya fito? Kuma suna ina ne Sani Danja ya fitar da Fim dinsa na MAI BABBAR RIGA ? Tabbas lokaci yayi da al'umma zata zabawa kanta mafita ko dai ta bi hanyar Allah SWT wadda yake fawwalawa wasu daga bayinsa wadanda ya zaba su bayyanawa mutane mafita ko kuma su hadu da mutanen Fir'auna da Abu jahil a matattara guda.
Naji ance gwamnatin Kano wai ta dakatar yin Fina-finan batsa na hausa har tsawon shekara guda, amma gidajen rediyo mallakarta suna nan suna dada tallan wadannan fina-finan batsa na hausa ta hanyar sanya wakokin batsar da suka yi a baya. Shin jagoran Gwamnatin jihar Kano bai san da yunkurin da almajiran Malamin nan na Zariya suka yi ba na yin Fim din Shehu Usman Dan Fodio ba ne ba? Idan ya sani wace irin gudumowa ya bada a matsayinsa na wanda ya amfani jihadin Shehu? Mu ma 'Yan Tijjaniyya muna binsa bashi domin muna da hakkin ya sa ayi mana Fim din Shehu Tijjani domin Malamanmu sun tare a gidansa suna kwadayin abin duniya, har suna zuga shi wai 'Yan Kadiriyya sun zama Shi'a.
Shawarata ga babban yayana Malam Ibrahim Shekarau itace ya ruguza harkar Fina-finan batsa na hausa har abada, kuma ya hana wakokin soyayya irin nasu har abada, sannan ya nemi mutane masana addini su kirkiri wani abu wanda zai maye waccan muguwar sana'a irinta mutanen Annabi Ludu, kuma ya hana shirin da Ibrahim Mandawari yake gabatarwa a gidan rediyon Freedom dake Kano na Fina-Finan hausa wanda yake taimakawa wajen yada wancan fasadi, kuma yayiwa Allah da Manzonsa ya kai ziyara Sokoto domin sulhunta al'ummar musulmi ya taimaki masu gaskiya ya kuma yiwa marasa gaskiya fada ya kuma taimaki wadanda aka konewa dukiya da gidaje domin shi dai na Allah ne, kuma saboda haka jama'a suka zabe shi domin kullum yana fadin Allah.
RABIU YUSUF
08065273401

YAN FIM SUN FI MALAMAI

Edita ina muku sallama ta addinin musulunci ke da abokan aiki da masu karatu, wato, Assalama alaikum.
Bayan haka edita na karanta hirar Ibro da kuka buga a mujallar Fim mai farin jini inda har Ibro yake cewa sun fi Malamai fadakarwa su 'yan Fim, wannan magana ta Ibro haka take babu ja domin Ibro ya fadi wannan magana ne bisa sani ba wai bisa son zuciyarsa ba.
Abin daya sa na fadi haka kuwa har nake jinjina ga shi Ibro shi ne da farko dai shi Ibro yana nufin "Ulama'u Suki" wato Malamai masu harkar kasuwanci da ayoyin alkur'ani wadanda suke raba kan al'ummar musulmi ta hanyar kungiyoyinsu mara sa amfani ga addini. Malamai wadanda suke rabon kaulasan wato suke kafirta mutanen da suka shaida babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah (swt) kuma Muhammadu (sawa) Manzon Allah ne, sannan suka tsaida salla suke kuma bada zakka, wanda Manzon Allah (sawa) ya ce duk wanda ya aikata haka mutuncinsa da jininsa ya kubuta al'amarinsa yana hannun Allah. Amma irin wadancan malamai suka ce ba haka ba, domin kuwa da sun yarda da haka da sun tsaya akan wannan magana ta Manzon Allah (sawa) domin kuwa Allah (swt) da kansa yake fadin duk mutumin da yayi imani da Allah (swt) yake kuma fatan ya hadu da Allah lafiya a gobe kiyama to abin koyinsa shine Annabi Muhammadu (sawa). Shin yanzu irin wadancan malamai da suke kafirta musulmi mai salla mai taimakawa 'yan uwansa da dukiyarsa da wa suke koyi kenan? Domin Manzon Allah (sawa) bai cutar da larabawa ba wadanda ya tarar dasu sun fi kowa kafirci a duniya a lokacin bayyanarsa, domin ya samu larabawa suna binne 'ya'yansu mata da ransu, kuma suna kwace da fashin dukiyoyin jama'a tare da sanya mataye rawa tsirara da sunan bauta, ruwan giya kuwa shi ne ruwan shan su mushe kuwa abin kalacin su, karuwai kuwa har tuta suke sawa a samun dakunansu, sannan uwa uba gumaka dari uku da wani abu ne a dakin Ka'aba da su larabawa suke bautawa, amma Manzon Allah (sawa) dan Abdullahi mai kira abi Allah (swt) wanda karya bata hada hanya da shi, Allah (swt) ya tashe shi a cikinsu ya kuma kira su zuwa ga hanyar Allah (swt) ta hanyar kira mai cike da girmama dan Adam ba tozarta shi ba ko wulakanta shi ba, wanda hakan ya sanya hatta manyan kafiran Makka suna kiran Manzon Rahama (sawa) da Al-amin wato mai gaskiya da amana.
Da Malamanmu sun tsaya akan koyarwar Manzon Allah (sawa) sun watsar da baiwa mata rubutu su wanke gabansu dashi, sun watsar da yiwa matan aure ciki a makarantun Islamiyyoyi, sun watsar da yin sihiri da ayoyin alkur'ani mai girma suna raba uba da dansa, uwa da danta, suna sanya gaba tsakanin miji da matarsa, sun daina bi ofisoshin gwamnati ana basu na kalaci, sun daina baiwa 'yan siyasa layu suna kwana tsirara a makabartu, sun dawo akan hanyar gaskiya hanyar kira zuwa ga Allah (swt) ba hanyar tara mutane ba su sanya su a hanyar siyasar dimokaradiyyar Amurka bayan sun sace musu imaninsu, to wallahi da babu wani ko wata yarinya da zata baro kauyansu ta shigo garin Kano da sunan a sanya mata abin daukar hoton bidiyo tana karya kwankwaso ita da namiji baligi da sunan neman abinci. Wanda masu yin hakan dama su sun sallama kansu a matsayin fitsararu masu kangarewa Allah (swt) da Manzonsa (sawa) domin su basu kira kansu masu bin tafarki ba, wanda ko a lahira wutar mai munafunci da wasa da izgilanci da cin abinci da ayoyin Allah (swt) ta fi ta wanda yake aikata sabonsa da rashin sani ko jahilci.
Ina so mutane su yi adalci kuma su bude kwakwalensu su fadi gaskiya a tsakaninsu da Allah (swt) su duba su gani da 'Yan Fim da malamai su waye suka fi fadakar da al'umma mu dauke son zuciya mu fadi gaskiya domin gaskiya ko ta kare ce ka bashi kayansa. Mu duba muga irin bala'in da kaskancin da muke ciki a yau su waye suka jawo mana "yan fim ko Malamai? Idan baku sani ba to ga tambaya su waye suke halasta aure akan aure? Su waye suke gyaran aure saki? Su waye suke cewa dan kungiya kaza kafiri ne? Su waye suke karbar kudin daurin aure idan suka kulla aure? Su waye suke cin dukiyoyin marayu a gidajen mutuwa da sunan suna yiwa mamatansu addu'a? Su waye suke boye ma'anonin gaskiya na ayoyin Allah (swt) su sanya son zukatansu? Su waye suke suke siyasar dimokaradiyya da addini a halin sun san ba a dora ginshikin gini akan iska? To amsar idan baku sani kuce Malamai masu ciniki da ayoyin Allah (swt) wandanda suke kirkirar karya su jingina ga Allah (swt).
Idan dan Fim yana aikata daya daga cikin wadancan abubuwa dana fada ku fada mini. Kuma idan dan fim ya taba fitowa yace shi na Allah ne ku zo ya wuce muku gaba ku fada mini?
A yau ta hanyar sana'ar Fim din Hausa wadda take da cibiya a Kano mutane da yawan gaske sun iya warware matsalolin zamantakewar su da matansu da 'ya'yansu da iyayensu da makwabtansu kai har ma da wadanda ba addininmu daya dasu ba wannan sana'a ta Fim din Hausa ta wayarwa da jama'a da yawan gaske kai, inda zaka ga mace ta koyi yadda zata yiwa mijinta magana cikin ladabi, wata kuma ta koyi yadda zata zauna da iyayen mijinta da 'yan uwansa, wata kuwa ta hanyar Fim din Hausa ta fahimci dalilin da mijinta yake dadewa a hirar dare ta kuma gyara kuskurenta cikin sauki. Ba wai mata kawai ne ba suka fa'idantu da wa'azantarwa da suke cikin Fina-finan Hausa ba har ma da mu maza wanda muke aikata miyagun ayyuka mun ga karshen yadda masu neman 'yan mata yake zuwa musu da nadama, mun ga karshen masu kin taimakawa dangin su da 'yan uwansu duk masu Fina-finan Hausa din nan sun nuna mana ta hanyar sana'arsu kuma ya kasance darasi da wa'azi agaremu domin idan bai faru da kai ba to ya faru ga wani ka gani.
Mu koma ga Littafin da ya fi kowane littafi muhimmanci da daraja da girma wato alkur'ani mai girma wanda da shine muke fahimtar addini kuma shine littafin daya tattara kome da komai na illimi, wanda ina ji fiye da kashi biyar cikin goma na alkur'ani mai girma labarai ne na mutane da alkaryu iri-iri da suka gabata Allah yake bamu domin mu shiga taitayinmu wanda duk mai imani idan ana karanta masa alkur'ani kasancewa yake yi tamkar ana nuna masa abin ne a cikin zuciyarsa. Sannan duk irin kirkinki ka idan kana karanta alkur'ani zaka ji labarin wanda ya fi ka nagarta da kirki haka nan duk iya shegenka zaka ji wanda ya fi ka kuma kaji yadda Allah (swt) mai kowa mai kome yayi da shi, wanda ta haka za ka zabawa kanka inda kake son shiga a gobe kiyama. Haka nan ma suma ma masu Fina-finan Hausa labari ne suke badawa wanda a karshe zaka ga makomar wanda aka gina labarin akan sa idan azzalumi ne zaka gani, idan mutumin kirki ne shima zaka gani karshensa. Inda cikin hikima suka dunkule maka rayuwa a cikin awa biyu ko kasa da haka kuma suka sanar da kai yadda take wanda duk jahilcinka dole ne ka fahimci abin da ake nufi domin dai da yarenka aka shirya Fim din konace wa'azin. Ko bamu ga yadda abokan zamanmu suke yada manufofin addinin su ba ta hanyar fina-finan su ba, wanda kuma yake samun tasirin gaske a tsakaninsu
Sannan kuma akwai bambamci tsakanin wa'azin malaman zamani da wa'azin masu fina-finan zamani da farko dai mai wa'azin zamani duk mutumin da fahimtarsa ta saba da tasa a wajensa idan yayi masa da sauki ya kira shi kafiri. Sannan kuma mai wa'azin zamani kome ya sani, baya tunawa da cewa kome kake akai akwai sama da kai idan ba haka ba ta yaya zai kira mai yawaita fadin kalmar La'ilaha illallah Muhammadur Rasulillah, mai yawan salatin Manzon Allah (sawa) kuma mai yawan tuba izuwa ga Allah (swt) kafiri saboda yayi imani da abin da yake yi. Wanda babu wani dan Fim ko ince mai shirin fina-finan hausa da zai yi haka a hanyar fina-finansa. Kuma duk tsiyar mai shirin Fina-finan Hausa ba za ka taba jin ya sauya fassara littafin Allah (swt) ba domin ya biyawa wani bukatar sa ba, shi dai ka bar shi akan sana'arsa ta Fina-finan Hausa kawai wadda jama'a suke amfana da kokarinsa ko ince wa'azinsa. Karshen mai tabara da iskanci a wasan Hausa ba sama da Ibro, amma ban taba jin an kira sunan Manzon Allah (sawa) ba a cikin wasan Ibro ba tare da Ibro yayi salati ga Manzon Allah (sawa) ba, kuma naga mutumin daya haddace hadisan Manzon Allah (sawa) masu yawa ta hanyar Fina-finan Ibro wanda Malam Dare yake kawowa a duk Fim din Ibro.
Sannan mai shirin fim idan dan iska ne masu kallo sun sani domin shigarsa da kalmar bakinsa ta isa su yi masa hukunci domin babu munafunci a tare da shi, ya rage na mai kallo ya san na dauka yasan na jefarwa. Amma malamin da zai fada maka Allah a bakinsa amma a zuciyarsa babu Allah kuma idan ya ganka baka san inda aka dosa ba sai yayi ta wasa da kwakwalwarka, har wata rana kaji mutum yana kiran kansa shi Allah ne an bashi wuridi ya samu motsuwa, Allah ka tsare mu! Amma dan Fim iyakaci ya mai da kai mai rawa a cikin jama'a idan ka dauki hanyar fitsararun masu fim kenan, ko su mai da ke mai yawo tsirara a gari ta hanyar sa suturar banza idan baki san mutuncin kanki ba. Amma karya ne mutum yace ya koyi shaye-shaye ta hanyar fim din Hausa ko ya koyi munafunci ta hanyar fim din Hausa ko ya koyi kafirta dan uwansa musulmi ta hanyar fim din hausa.
A karshe ina kira da mutanen da suka jahilci maganar Ibro da yace su masu fim sun fi Malamai fadakarwa su fahimci abin da Ibro yake nufi kuma su yi masa adalci wajen yi masa kyakkyawar fahimta. Sannan kuma su lura da cewa sai Malamai sun bar koyarwar Manzon Rahama (sawa) ne al'umma take fadawa cikin bala'i da masifu iri-iri domin aikin da masu fim din hausa suke yi aiki ne na malamai wanda suka watsar suka kama business da addini sai da azumi su kama aikin da ya dace ace a tsawon shekara shi suke yi. Mu duba mu gani a garin Kano musamman gidajen Malamai masu kafirta al'umma zamu ga duk abin da tattaciyar mara kunyar 'yar fim take yi shi suma 'ya'yansu daya dace su zama abin koyi suke aikatawa, ku je jami'o'i da makarantu ku gani.
Malamai ku ji tsoron Allah (swt) ku daina kwadayi ku tsaya kyam akan tafarkin Allah (swt) domin ku ne kuka lalace shi yasa matasanmu suka nemawa kansu hanyoyin da suke ganin sune mafita a tare da su a halin kuwa hanyoyin halaka ne suka fada. Tabbas al'umma zata gyaru idan har Malamai suka yi aiki tsakani da Allah (swt) hatta fina-finan nan da 'yan Jos da Kaduna suke ta kwararowa jihar Kano suke abin da suka koya a gidajensu wanda su a tarbiyyarsu haka shine daidai idan Malamai na Allah suka shiga wannan harka fina-finai lalle za su tsarkake harkar kuma wannan zai rage musu aiki wajen isar da Sakon Allah (swt) ga 'yan uwanmu na kasa daya wadanda har yanzu ba a samu masu kai musu addinin Allah (swt) ba ta hanyar da zasu fahimce shi ba wanda a kullum burinmu mu kira su da miyagun sunaye na arna ko muce da su arnaku wanda abin da suke na sabo da kannenmu suke yi ko yayyenmu ko mu da kanmu, suturar da matar da ba musulma ba kuma tattaciyar 'yar banza a cikin wadanda ba musulmin zata sanya ita 'yar musulmi ayau take sanyawa, ayau 'ya'yan musulmi sune masu layi a gidajen shan giya inda zaka ga wanda ba musulmi ba ya sha kwalba daya ya hakura amma sai kaga dan musulmi ya sha katan guda ya kara madarar sukudaye ko wiwi, haka 'ya'yan wadanda ba musulmi ba ayau sune 'ya'yan musulmi suke zinace zinace da su kuma idan magana ta tashi sai muce musu arna a halin abin da suke aikatawa shi 'ya'yan musulmi suke aikatawa.
kirana na karshe ga shugabannin masu harkar fina-finan Hausa na Kano wanda daga masu kiran kansu jikokin Manzon Allah (sawa) sai wanda suke 'ya'yan malamai da Manyan limamai da sauransu da su yiwa Allah da Manzonsa su kawo gyara a cikin wannan sana'a tasu wadda da ita za su iya jihadi mai fadin gaske da ita fiye da dukkan wani abu da wani Malami zai yi a wannan lokaci, domin mata da yara da manya dukkansu suna kaunarsu tare da basu lokutansu wajen sauraran abin da suke kokarin isarwa.
RABIU HAMDALA

8.11.07

MAFARKIN SHABBAKIN MANZON ALLAH SAWA

KIN MANZON SALAM.
Bayan haka ina yiwa al'ummar musulmi masoya Manzo Muhammad SAWA da Iyalansa tsarkaka a duk inda suke a duniya fatan alheri, musamman 'yan uwana 'yan darikar Tijjaniyya ta Maulanmu Shehu Ahmad Tijjani RTA da kuma masoyanmu masu kaunarmu a duk inda suke.
Bayan haka yau Litinin 26-10-1428 (5-11-2007) da daddare da misalin karfe 2:00 na dare ina barci sai nayi mafarki da Shabbakin Manzon Allah SAWA da yake garin Madina, inda na ganni a bakin Shabbakin a tsaye wasu mutane fararen fata suna zuwa domin suyi ziyara ga Manzon Allah SAWA ana korarsu idan suna yin addu'o'i a wajen, inda shi mai kula da wajen wanda bakar fata ne kuma yana magana da harshen Hausa, yake nuna mini wadannan mutane suna yin wani abu ne mara kyau, a halin ba abin da suke yi sai tawassilli da Manzon Allah SAWA. A lokacin dana kusancin makwancin Manzon Allah SAWA sai na leka ta wata kofa inda naga Kabarinsa mai albarka da kwarjini, sannan a gefen kabarin akwai wasu kabararruka kana guda uku wanda basu kai na Manzon Allah SAWA girma ba, su wadannan kananan kabararruka sai na ga shi wannan mutumi mai kula da wajen yana diban wasu sarkoki na gwalagwalai yana yi musu ado da su amma bai kula da na Manzon Rahama SAWA ba. A lokacin da nake leka kabarin Manzon Allah SAWA ta cikin wasu kananan kofofi sai nake fadin,"ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL FATIMA ZAHARA'U ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL KASIM ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL ZAINAB ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL UMMUL KULSUM!..... ......... ."
Haka na ganni ina ta yiwa Manzon Allah SAWA kirari da salati, har sai dana ga kabarinsa yana dada girma yana yin numfashi kamar kabarin zai bude ya fito. A lokacin da wannan mai kula da kabarin ya ga halin da nake ciki wanda har na fita daga hayyacina saboda kirarin da salati da nake yi masa SAWA a gaban kabarinsa SAWA, sai wannan mai kula da waje ya kama ni ya damkawa wani askari ni, wato sojan kasar Saudiya, wanda shi kuma ya rike hannayena guda biyu ya tafi dani wajen shugabansa wanda shi kuma ya umarce shi daya kai ni wani waje da suke azabtar da mutane. A lokacin sai wannan soja yake duka na da wani abu mai kama da bindiga, amma sai nake ji kamar yana shafata da wani abu mai tsananin taushi banji alamar wani ciwo ko zafi ba.
A lokacin da wannan askari yake kokarin tafiya dani sai nake masa magana da harshen turanci al'amarin daya jawo dimbin jama'ar da suke zaune a cikin masallacin suka saurari tambayar da nake yiwa wannan askari, kuma suka zaku su ji tambayar da nake yi masa da amsar da zai bani.
Na tambayi wannan askarin cikin harshen turanci shin bani da iko in bi mazahabar da nake ganin itace ta dace na bita, kuma na aiwatar da ayyukan ibadata daidai da fahimta ta?
A lokacin da nake tambayar wannan askarin sai yake kokarin ya hana ni karasa tambayata saboda ya hana mutane su fahimci wane ne mai gaskiya a tsakani na da shi, inda yake fada mini wai limaminsu Sudais ma'asumi ne don haka kawai in bi hanyar limamansu.
A lokacin da wannan askari ya gaza hana jama'a fahimtar abin da nake son fada har jama'a suka fahimci abin da yake faruwa sai kawai naga jama'a bakaken fata da suke wajen wanda akasarinsu talakawa ne masu kananan sana'o'i irin sai da lemon zaki, sun watsar da kayan sana'arsu sun nufo inda nake, suma mata wanda na gansu cikin shiga irin ta matan 'yan uwa musulmi almajiran Malam Zakzaky sanye da hijabi wanda suma suka baro wajen da suke a zaune a masallacin suka nufo inda nake inda na gansu dubunnai suna fadin, "ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH !!"
Wannan askar da sauran 'yan uwansa suna ganin yadda mutanen nan suka kawo mini tallafi sai ya sake ni ya nemi sulhu dani.

Wannan shine mafarkina wanda nayi kuma dama wani abu makamancin haka ya taba faruwa da ni a lokacin dana je aikin Hajji a shekarar 2000.
Allah ya kara mana son Manzon Allah SAWA da Iyalansa tsarkaka da masoyansu ko da kuwa muna da bambamcin fahimta dasu matukar dai su masoyan Manzon Manzon Allah SAWA ne da Iyalansa tsarkaka.
Wannan mafarki nawa yana dauke da babban sako ga mai hankali.
Daga,
Rabiu Yusuf Kano,